Close Menu
  • Home
  • E News
  • Bollywood
  • Hausa series
  • kannywood
  • Tech
Facebook X (Twitter) Instagram
Hausaloaded
  • Home
  • E News
  • Bollywood
  • Hausa series
  • kannywood
  • Tech
Facebook X (Twitter) Instagram
Hausaloaded
Home » Attahiru Bafarawa ya rubuta wasika ga Shugaba Buhari
NEWS

Attahiru Bafarawa ya rubuta wasika ga Shugaba Buhari

iGeekBy iGeekSeptember 28, 2016No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email
– Tsohon gwamnan jihar Sokoto a karkashin Jam’iyyar All Nigeria Peoples Party (ANPP), Attahiru Bafarawa
– Bafarawa tsohon gwamna ne a Jam’iyyar ANPP, wanda daga baya zama cikin Shugabannin ta, itace kuma Jam’iyyar da ta far aba Shugaba Buhari tikitin tsayawa takara a kasar nan

Advertisements

Shi kan sa Attahiru Bafarawa, ya taba neman takarar Shugabancin Kasar a karkashin Jam’iyyar DPP. Bafarawa ya rubuta budaddiyar wasika zuwa ga Shugaban Kasa Muhammadu Buhari game da yadda zai samu nasara a mulkin sa. Idan ba a manta ba, Attahiru Bafarawa yana cikin iyayen gidan Jam’iyyar APC lokacin da aka kaddamar da ita, sai dai, daga baya ya fice abin sa.
Alhaji Dalhatu Attahiru Bafarawa yace wannan ne karo na hudu da ya rubuta wasika zuwa ga Shugaban Kasar Najeriyar, Muhammadu Buhari. Sai dai wannan karo Attahiru Bafarawa yace ya rubuta wasikar ta sa a bude. A cewar tsohon Gwamnan dai Kasar na fama da tarin matsaloli, don haka dole a sa hannu gaba daya wajen ceto Kasar.
Attahiru Bafarawa yaba Shugaba Buhari shawarar cewa ya duba wajen Jam’iyyar sa ta APC domin neman wadanda za su iya kawo karhsen matsalar da Kasar ta ke ciki. A cewar sa bah aka Shugaba Jonathan yayi ba, kuma bai zargi shugabannin baya ba. Bafarawa yace dole Buhari ya rika matso da Gwamnonin adawa jika, duba da irin yadda Shugaba Obasanjo yayi da Gwamna Bakura na Zamfara a lokacin sa. Yace dole kuma Buhari ya rika karbar shawara dage mutane da dama, musamman wadanda suka taimaka masa ya samu wannan matsayi.
Attahiru Bafarawa ya kuma kira Shugaba Buhari da ya karfafa Hukumar EFCC domin yaki da rashawar ya fi da. Kuma idan abin da gaske ne, a binciki ‘Yan Jam’iyyar sa ta APC, musamman wadanda suka tsero cikin ta don samun mafaka.
Tsohon Gwamnan Jihar Sokoton, Attahiru Bafarawa yace dole Buhari ya shirya jin suke daga bakin Jama’a duk kuwa dacin hakan.
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
iGeek
  • Website

Related Posts

President Buhari Signs Proclamation Proscribing IPOB

September 19, 2017

Full Text Of President Buhari’s Address At The 72nd United Nations General Assembly | READ

September 19, 2017

BREAKING NEWS:- Two Suicide Bombers Storm Borno, 15 People Killed

September 18, 2017
Leave A Reply Cancel Reply

Recent Comments
  • fbdownloader on Download Nura M Inuwa Full Wedding video part 3 2017
  • Muhammad on MUSIC : Umar M Shareef – Tsohuwata Zuma
  • Unknown on MUSIC : sayyad Gadon Kaya – Shakuwa A So
  • Abubakar Rabiu on [MTN]Yadda Zaka Samu Free 1GB Data A Layin Mtn
  • IBRAHIM BELLO GIDADO on Lastest song Rarara again TALEKO TA LABE MP3
Facebook X (Twitter) Instagram Pinterest
  • About Us
  • Contact Us
  • Disclaimer
  • Privacy Policy
© 2025 ThemeSphere. Designed by ThemeSphere.

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.