Close Menu
  • Home
  • E News
  • Bollywood
  • Hausa series
  • kannywood
  • Tech
Facebook X (Twitter) Instagram
Hausaloaded
  • Home
  • E News
  • Bollywood
  • Hausa series
  • kannywood
  • Tech
Facebook X (Twitter) Instagram
Hausaloaded
Home » SHIN SAYYIDINA UMAR YA TABA BINNE 'YARSHI ?|DR JAMILU YUSUF ZAREWA
FATAWA

SHIN SAYYIDINA UMAR YA TABA BINNE 'YARSHI ?|DR JAMILU YUSUF ZAREWA

iGeekBy iGeekNovember 27, 2016No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

SHIN SAYYIDINA UMAR YA TABA BINNE ‘YARSHI ?


Tambaya :
Assalamu alaikum malam, shin don Allah ina gaskiyar lamarin da ake cewa : Umar yana kuka wataran kuma sai a ga yana dariya, har aka tambaye shi, sai yake cewa : ya tuna ‘yarsa da ya rufe a zamanin jahiliyya shi ne yake kuka ?

Amsa :
To dan’uwa tabbas wannan maganar ta yadu a wajan masu wa’azi da masu huduba akan minbarai, saidai ba ta da tushe, kuma karya ce, saboda abubuwa kamar haka :


1. Masana tarihi sun tabbatar da cewa : matar Umar R.A ta farko a rayuwarsa, ita ce Zainab ‘yar Maz’un wacce ta Haifa masa Hafsan da Annabi s.a.w. ya aura, don haka Hafsa ita ce babbar ‘yarsa, kuma da ita ake masa alkunya, don haka idan bai rufe babba ba daga cikin ‘ya’yansa, ta yaya zai bunne wacce ta zo daga baya ?, tare da cewa :
ita kan ta Hafsan an haife ta ne kafin a aiko Annabi s.aw. da shekara biyar, ka ga kenan abin da ta riska na jahiiliyya ba shi da yawa .


2. Wacce ake cewa Umar ya bunneta da ranta, gaba daya littatafan tarihi ba su fadi labarinta ba, ko su kirga ta a cikin ‘ya’yansa ba.
3. Sannan kabilar Adiy wacce Umar ya fito daga cikinta ba su shahara da binne ‘ya’ya mata ba, a zamanin jahiliyya.


4. Dogon bincike ya nuna cewa : babu wannan kissa kwata-kwata a cikin littattafan Ahlussunah, asalinta daga littatafan ‘yan shi’a aka cirota, don haka su ne suka kirkire ta, dama kuma sun saba yin kage ga sahabban Annabi s.aw.


Allah ne mafi sani .

Don neman Karin bayani duba : Dirasa nakdiyya fi shaksiyati Umar 1/111. ﺩﺭﺍﺳﺔ ﻧﻘﺪﻳﺔ ﻓﻲ ﺷﺨﺼﻴﻴﺔ ﻋﻤﺮ ﺑﻦ ﺍﻟﺨﻄﺎﺏ ﻭﺳﻴﺎﺳﺘﻪ ﺍﻹﺩﺍﺭﻳﺔ 1/111 –

 Amsawa
 Dr jamilu zarewa
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
iGeek
  • Website

Related Posts

Yawun Bakin Budurwa Yana Kara Karfin Hadda Al-kur'ani inji Sheikh Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

March 12, 2018

Khudubar Ranar Juma'a Mai taken Sulhu Alheri ne Dr Muhammad Sani Umar R/lemo

February 18, 2018

[Audio] Download Raddi Mai Taken 'Babban Bola' ? Sheikh Bello Yabo Sokoto

July 24, 2017
Leave A Reply Cancel Reply

Recent Comments
  • fbdownloader on Download Nura M Inuwa Full Wedding video part 3 2017
  • Muhammad on MUSIC : Umar M Shareef – Tsohuwata Zuma
  • Unknown on MUSIC : sayyad Gadon Kaya – Shakuwa A So
  • Abubakar Rabiu on [MTN]Yadda Zaka Samu Free 1GB Data A Layin Mtn
  • IBRAHIM BELLO GIDADO on Lastest song Rarara again TALEKO TA LABE MP3
Facebook X (Twitter) Instagram Pinterest
  • About Us
  • Contact Us
  • Disclaimer
  • Privacy Policy
© 2025 ThemeSphere. Designed by ThemeSphere.

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.