Close Menu
  • Home
  • E News
  • Bollywood
  • Hausa series
  • kannywood
  • Tech
Facebook X (Twitter) Instagram
Hausaloaded
  • Home
  • E News
  • Bollywood
  • Hausa series
  • kannywood
  • Tech
Facebook X (Twitter) Instagram
Hausaloaded
Home » Gwamnatin Tarayya Za Ta Bude Makarantu Na Musamman Saboda Matan Aure
NEWS

Gwamnatin Tarayya Za Ta Bude Makarantu Na Musamman Saboda Matan Aure

iGeekBy iGeekJune 1, 2017No Comments1 Min Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Gwamnatin tarayya ta ce za ta bude makarantu na musamman saboda matan da aka cire daga makaranta saboda a yi masu aure.

Ministar harkokin mata Aisha Alhasan ita ta bayyana haka ga manema labarai a yau Alhamis a jahar Katsina, inda ta ce makarantun za su baiwa matan damar komawa makaranta daga gidajen mazajen su.

Ta ce za a bude makarantun a matakai guda biyu saboda kar a samu matsaloli.

Mataki na daya na wadanda suka bar makarantun sakandire ne kafin su kammala, mataki na biyu kuma na yaki da jahilci.

Ta bayyana cewa za a bude makarantun yaki da jahilcin a kowacce karamar hukuma a fadin kasar nan.

Haka kuma banda darusussuka da matan za su na dauka, za a koya masu sana’o’i kamar su dinki, hada man shafawa, sabulu, lemon sha, kyandir da sauran su.

Ministar ta yi kira ga malamai da shugabannin gargajiya da su baiwa gwamnati hadin kai wajen cimma manufofin ta na ilimantar da mata, saboda ya na da matukar muhimmanci.
Daure ka/ki yi sharhi:

Advertisements

Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
iGeek
  • Website

Related Posts

President Buhari Signs Proclamation Proscribing IPOB

September 19, 2017

Full Text Of President Buhari’s Address At The 72nd United Nations General Assembly | READ

September 19, 2017

BREAKING NEWS:- Two Suicide Bombers Storm Borno, 15 People Killed

September 18, 2017
Leave A Reply Cancel Reply

Recent Comments
  • fbdownloader on Download Nura M Inuwa Full Wedding video part 3 2017
  • Muhammad on MUSIC : Umar M Shareef – Tsohuwata Zuma
  • Unknown on MUSIC : sayyad Gadon Kaya – Shakuwa A So
  • Abubakar Rabiu on [MTN]Yadda Zaka Samu Free 1GB Data A Layin Mtn
  • IBRAHIM BELLO GIDADO on Lastest song Rarara again TALEKO TA LABE MP3
Facebook X (Twitter) Instagram Pinterest
  • About Us
  • Contact Us
  • Disclaimer
  • Privacy Policy
© 2025 ThemeSphere. Designed by ThemeSphere.

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.