Hukumar EFCC ta sake gano wani katafaren shago a Babban birnin tarayya Abuja mallakar Uwargidan Tsohon Shugaban Kasa, Patience Jonathan wanda aka kiyasta kudinsa a kan Naira Bilyan Shida.
Advertisements
Rahotann sun nuna cewa Uwargidan tsohon Shugaban ta mallaki shagon ne ta hanyar amfani da Gidauniyarta mai suna ” Aribawa Aurera Reach Out Foundation.”. A halin yanzu dai, EFCC ta nemi wasu Bankuna takwas da aka yi amfani da su wajen biyan kudin gidan kan su gabatar mata da cikakken bayani.