Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Hausaloaded
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Hausaloaded
    Home » Yansanda sun kama mai fataucin sassan mutum a jihar Kebbi
    NEWS

    Yansanda sun kama mai fataucin sassan mutum a jihar Kebbi

    iGeekBy iGeekMay 19, 2017No Comments2 Mins Read
    Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
    Share
    Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email


    – Yansanda a jihar Kebbi sun cika hannu da wani mutumi daya kware wajen hakar kaburbura yana sace gawa

    – Mutumin yace talauci da halin matsin rayuwa ne ya shigar da shi wannan harka

    Jami’an hukumar yansandan jihar Kebbi sun cika hannu da wani mutumi daya kware a sana’ar ciro gawa daga kabari, kuma ya yanke sassan jikinta don fataucinsa a garin Bagudu na jihar Kebbi.

    Kwamishinan yansandan jihar, Ibrahim Kabiru ya bayyana haka yayin dayake ganawa da yan jaridu a ranar Alhamis 18 ga watan Mayu, inda yace sun samu nasarar kama mutumin ne bayan samun wani rahoton sirri, inji rahoton kamfanin dillancin labaru, NAN.

    Advertisements

    Kwamishinan yace da misalin karfe 3:30 na dare ne suka kama mutumin a makabartan Kaoje yayin dayake kokarin hako wani gawar bawan Allah don siyar da sassan jikinta.


    Kwamishinan ya kara da fadin, mutumin ya amsa laifinsa, kuma ya fallasa mutumin daya daura shi a harkar, mai suna Malam Muhammadu dake zama a jihar Sakkwato, inda shi mutumin ke kai katako kafin ya shiga wannan harkar.

    Daga karshe dai mutumin ya nemi afuwa, inda yace talauci ne ya sanya shi yin wannan mummunar aiki, tare da burinsa na ganin ya kula da iyalinsa.

    A wani labarin kuma, NAIJ.com ta gano yansanda sun kama wani fasto mai shekatu 55 mai suna Alimi Isaiah dauke da kawunan mutane da wasu kayan tsafe tsafe a jihar Ogun.

    ©naij.com

    Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
    iGeek
    • Website

    Related Posts

    Mai Boutique Ya Fitar da Wraps 127 na Kwayar Cocaine Bayan Komowa Daga Thailand

    October 13, 2025

    Mahmood Yakubu Ya Gane Fasaha Ta Inganta Zabe Amma Ba Za Ta Iya Kawar Da Matsalolin Siyasa Ba

    October 13, 2025

    Kungiyar Malaman Kudu ta Kaduna Ta Nemi Sanata Katung Ya Bar PDP, Ya Shiga APC Don Ci Gaban Yankin

    October 13, 2025
    Leave A Reply Cancel Reply

    Recent Comments
    • Nasiru sambo on MUSIC : sayyad Gadon Kaya – Shakuwa A So
    • Nasiri sambo on MUSIC : sayyad Gadon Kaya – Shakuwa A So
    • fbdownloader on Download Nura M Inuwa Full Wedding video part 3 2017
    • Muhammad on MUSIC : Umar M Shareef – Tsohuwata Zuma
    • Unknown on MUSIC : sayyad Gadon Kaya – Shakuwa A So
    Facebook X (Twitter) Instagram Pinterest
    © 2025 ThemeSphere. Designed by ThemeSphere.

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.